Taskar Labarai

Hukumar Hisbah Ta Kama Murja Ibrahim Kunya

Hukumar Hisbah Ta Kama Murja Ibrahim Kunya.

Shugaban Hukumar Sheikh Aminu Daurawa ya tabbatar wa TRT Afrika Hausa cewa za a gurfanar da ita ne kan tuhume-tuhumen yin bidiyon rashin tarbiyya a kafafen sada zumunta.

Hukumar Hisbah ta jihar Kano ta ce za ta gurfanar da fitacciyar ’yar TikTok Murja Ibrahim Kunya a gaban kotu.

Shugaban Hukumar Sheikh Aminu Daurawa ya tabbatar wa TRT Afrika Hausa cewa za a gurfanar da ita ne kan tuhume-tuhumen yin bidiyon rashin tarbiyya a kafafen sada zumunta.

Murja ta shahara musamman a shafukan sada zumunta inda take da miliyoyin mabiya, inda ake ganin tana yawan jawo ce-ce-ku-ce.

A shekarar 2023 ne wata kotu a Kano ta taɓa tura Murja da wasu yan TikTok zuwa gidan gyaran hali.

Ko a kwanakin baya sai da hukumar ta Hisbah gayyaci Murja domin ja mata kunne.

Haka ma a kwanakin baya Gwamnan Kano Abba Kabir Yusuf ya ce zai saka ta cikin jerin waɗanda za a yi wa auren zawarawa a Kano.

Related Articles

Back to top button